An kashe mutane uku a lokacin da suke yunkurin tserewa daga maboyar masu garkuwa da mutane a jihar Kogi.
Sanata mai wakiltar mazabar Kogi ta Yamma Sen Sunday Karimi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar Alhamis.
Ya yi kira ga kwamishinan ‘yan sandan jihar Kogi da daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da su magance matsalar rashin tsaro a garin Isanlu da ke karamar hukumar Yagba ta Gabas.
Dan majalisar ya koka da rashin tsaro a Isanlu, inda ya jaddada cewa, cikin sa’o’i 48, an yi garkuwa da mutane shida.