Gwamna Ododo ya bi layin zaɓen domin zaɓen maigidansa Yahya Bello

Gwamnan jihar Kogi, Usman Ododo a ranar Litinin ya shiga layin masu kaɗa kuri’a domin zaɓen wanda ya gada, Yahaya Bello a zaɓen fitar da gwani da aka gudanar na mazabar dan majalisar dattawa da zai wakilci mazabar Kogi ta tsakiya.

Bello wanda tsohon gwamnan jihar ne da ya shafe wa’adi biyu na neman jam’iyar APC ta tsayar da shi takarar sanata a zaɓen shekarar 2027.

A cikin wani  hoto da aka wallafa a shafin Facebook ya nuna Ododo akan layi inda yake dauke da katinsa na zaɓe.

Da yake bayani bayan ya kada kuri’arsa Ododo ya bayyana  cewa zaɓen na gudana lafiya ba tare da tashin hankali ba ya kara da cewa an bawa yan jam’iyyar ta damar zaɓen ɗan takarar da su ke so.

Yanzu haka dai Bello na fuskantar sharia a gaban babar kotu birnin tarayya Abuja inda ake tuhumar da almundahanar kuɗaɗe.

More from this stream

Recomended