
Yan bindiga sun sake kai hari kan al’ummar kauyen Dan Gulbi dake karamar hukumar Tureta ta jihar Sokoto ƙasa da kwanaki biyu bayan kai makamancin irin harin da ya jawo asarar rayukan mutane 17 ciki har da wasu baƙi da su ka kai ziyarar Sallah garin.
Mazauna garin sun bayyana cewa maharan da suka je garin akan babura sun farma ƙauyen da misalin karfe 08:00 na safiyar ranar Talata inda su ka riƙa harbin kan me uwa da wabi abun da ya tilastawa mutanen ƙauyen tserewa domin tsira da rayukansu.
Wata majiya dake kauyen ta yi zargin cewa mutanen da ba su gaza 20 ne ba aka kashe a yayin harin na bayan-bayan nan a yayin da aka ƙona gidaje da dama wasu kuma mutanen ba a san inda su ke ba.
Wani mazaunin ƙauyen da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce maharan sun isa kauyen ne a dai-dai lokacin da mutane suka taru a runfuna.
“sun zo suka fara harbin mu. Sai nutane sun fantsama su ka yi ta kansu domin tsira da rayukansu,” a cewar majiyar
A ranar Lahadi ne wasu gungun ƴan bindiga dake ɗauke da makamai su ka kai farmaki kauyen inda suka lashe mutane 17 tare da fasa akalla 20.
Yawan faruwar hare haren hakan ya sa mazauna kauyen suka nemi aka kawo musu ɗauki.

