Yadda Miliyoyin Mabiya Shi’a Ke Gudanar Da Tattakin Arbaeen A Karbala



Miliyoyin mabiya mazahabar Shi’a daga sassa daban-daban na duniya suna gudanar da tattakin Arbaeen a birnin Karbala na ƙasar Iraq domin tunawa da cika kwanaki 40 da kisan Imam Hussain, jikan Annabi Muhammad (SAW).

Ana gudanar da tattakin ne a ranar 20 ga watan Safar na kowace shekara, bayan cika kwanaki 40 da aka kashe Imam Hussain a ranar 10 ga watan Muharram.

A yammacin ranar 19 ga Safar, tawagogin mahajjata kan fara isa haramin Imam Hussain da na ɗan uwansa Abul Abbas domin gudanar da addu’o’i da nuna alhini kafin babban tattakin ranar Arbaeen.

More from this stream

Recomended