Mutane 18 yan jihar Sokoto sun mutu a wani hatsarin mota a jihar Kebbi

Mutanen da basu gaza 18 ne ba aka tabbatar da sun mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru akan hanyar Sokoto zuwa Yauri a jihar Kebbi a lokacin da suke dawowa daga jihar Lagos inda su ka je cirani.

Mutanen na daga cikin fasinjoji 20 dake cikin wata motar haya mai cin mutane 18 wacce taci karo da wata babbar mota da misalin ƙarfe biyu na daren ranar Litinin.

Wani shedar gani da ido da ya ziyarci wurin da abun ya faru ya faÉ—awa jaridar Daily Trust cewa fasinjojin na kan hanyarsu ne ta dawowa daga Lagos bayan da suka É—auki lokaci mai tsawo suna neman kuÉ—i akan

Bello Muhammad mamba a kungiyar sufuri ta NURTW wanda abokin direban motar ne ya ce ya shiga cikin al’ummar gari inda suka gudanar da aikin dauko gawarwakin bayan da suka samu labarin faruwar hatsarin.

Ya ce sun isa wurin da misalin karfe 04:00 na asuba ranar Talata inda suka tarar da motar tayi arangama da wata babbar mota.

A cewarsa an É—auki gawarwakin ya zuwa babban asibitin garin Yauri inda yan uwansu suka tantance su kafin a mika musu gawarwakin

More from this stream

Recomended