Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta yi na kama tsohon Gwamnan Jihar, Yahaya Bello a gidansa mai lamba 9, titin Benghazi, Wuse Zone 4, a gidansa da ke Abuja.

Jami’an hukumar yaki da cin hanci da rashawa sun mamaye titin ne da misalin karfe 9.30 na safiyar ranar Laraba inda suka killace gidan tsohon gwamnan, inda kuma suka hana zirga-zirgar mutane da ababen hawa.

Jami’an na EFCC dai sun samu tirjiya daga hannun ‘yan sanda sanye fa bakaken kaya.

Dan jarida wanda ya ziyarci gidan a ranar Laraba da yamma, ya lura da yadda jami’an EFCC dauke da muggan makamai, ‘yan sanda, jami’an ma’aikatar harkokin gwamnati, sashin yaki da ta’addanci da kuma jami’an tsaro na sirri suka taru a gidan na Yahaya Bello.

Bello dai yana fuskantar tuhum-tuhume ne saboda zargin cin hanci da rashawa lokacin da uake gwamna a Kogi.

More News

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naɗa Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...