Mahara Sun HaIIaka Jami’in NSCDC, Tare Da Sace Diyarsa Da Wasu Mutane A Kogi



Wasu mahara sun kashe wani jami’in Hukumar Tsaro da Kariya ta Fararen Hula (NSCDC), Ayo Olukotun, tare da yin garkuwa da diyarsa da wasu mazauna garin Odo-Ere, hedikwatar karamar hukumar Yagba West ta jihar Kogi.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe takwas da rabi na dare a ranar Litinin lokacin da maharan suka kutsa cikin garin tare da harbe-harbe, abin da ya jefa mazauna yankin cikin fargaba.

An ce daga bisani maharan sun kai hari gidan jami’in NSCDC, inda suka harbe shi kafin su yi awon gaba da diyarsa da wasu mutane zuwa cikin wani daji da ke kusa.

Majiyoyi sun bayyana cewa an garzaya da Olukotun zuwa asibiti bayan harin, amma likitoci sun tabbatar da rasuwarsa bayan isa cibiyar lafiyar.

Shugaban karamar hukumar Yagba West, Tosin Olokun, ya bayyana kisan a matsayin babban rashi ga iyalan mamacin da al’ummar yankin baki daya, tare da jajanta wa wadanda lamarin ya shafa.

Harin ya kara tayar da hankalin mazauna yankin kan matsalar tsaro, yayin da ake jiran matakan hukumomin tsaro domin kubutar da wadanda aka sace da kuma kamo wadanda suka aikata laifin.

More from this stream

Recomended