Tinubu Ya Umarci EFCC Ta Soke Umarnin Rufe Asusun Gwamnatin Osun


Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da ta koma kotu domin neman soke umarnin rufe asusun gwamnatin Jihar Osun.

Tinubu ya bayyana rashin jin daɗinsa kan matakin da EFCC ta ɗauka, musamman saboda lokacin da aka aiwatar da shi, yayin da jihar ke shirin gudanar da zaɓen gwamna.

Shugaban ya ce duk da cewa EFCC ta bi umarnin kotu, lokacin da aka ɗauki matakin na iya haifar da zargin cewa ana amfani da hukumomin gwamnatin tarayya wajen katsalandan a harkokin zaɓe.

Ya kuma jaddada cewa tun bayan hawansa mulki bai tsoma baki cikin ayyukan EFCC da sauran hukumomin bincike ba, domin ya ba su damar gudanar da ayyukansu cikin ’yanci.

EFCC ta samu umarnin kotu a ranar 5 ga Agustan 2026 na rufe asusun gwamnatin Osun, amma har zuwa lokacin wallafa rahoton ba ta bayyana cikakken dalilin neman umarnin ba.

More from this stream

Recomended