Ba kotu ya kamata ta tantance wadanda suka ci zabe ba – Jonathan

Goodluck Jonathan

Asalin hoton, Premuim times

Bayanan hoto,
Goodluck Jonathan

Tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan ya yi kira da a karfafa dokokin zaben kasar ta yadda takardar kada kuria kawai za ta tantance wadanda suka yi nasara a zabe, ba kotu ba.

Mista Jonathan ya jaddada cewa abin da aka saba a kai shi ne alhaki ya rataya a kan hukumomin zabe wajan dawo da ‘yan takara da bayyana wadanda suka yi nasara yayin da bangaren shari’a ke cikawa ta hanyar tabbatar da sakamakon da aka bayyana ko soke zaben da aka yi ba dai-dai ba da kuma ba da umarnin a sake zaben.

Ya ce : “Na riga na yi bayani a bainar jama’a a kan hakan don cewa takardar jefa kuri’a ba bangaren shari’a ba ne zai tantance wanda zai ci zabe ko kuma ya zabi shugabannin siyasa. Kamata ya yi takardar zaben ta kasance ita kadai ce tushen zabar shugabannin siyasa. “

An shigar da kararraki da dama a gaban kotu a kan lamuran da suka shafi fafatawa a tsakanin jam’iyyun.

A baya kotun koli ta soke zaben Emeka Ihedioha na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Imo .

Kotun ta kuma bayyana Hope Uzodinma na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara a zaben da aka yi a ranar 9 ga watan Maris na shekarar 2020.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...