Amaechi Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Atiku



Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya shigar yana ƙalubalantar zaɓen Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC.

Lauyan Amaechi, Jibrin Okutepa (SAN), ya bayyana wa kotu cewa an shigar da buƙatar janye ƙarar ne bayan ɓangarorin sun sasanta saɓanin da ke tsakaninsu. Daga nan ne Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta bayar da umarnin cire ƙarar daga gaban kotu.

Tun farko, Amaechi ya yi zargin cewa zaɓen fidda gwani na jam’iyyar ADC ya saɓa wa dokokin zaɓe da kundin tsarin mulkin jam’iyyar, inda ya buƙaci kotu ta soke zaɓen Atiku a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

More from this stream

Recomended