Atiku Ya Buƙaci Tinubu Ya Dakatar Da Gbajabiamila Domin Bincike





Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya buƙaci Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, domin ba da damar gudanar da cikakken bincike kan zarge-zargen cin hanci da rashawa da ake masa.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar, Atiku ya ce bai kamata gwamnati ta yi shiru kan zarge-zargen da ake yi wa Gbajabiamila ba. Ya kuma ce kamata ya yi a ba shi damar kare kansa ta hanyar bincike mai zaman kansa.

Atiku ya yi misali da yadda tsohon Shugaba Muhammadu Buhari ya dakatar da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, a 2017 domin gudanar da bincike kan zarge-zargen da ake masa, yana mai cewa bai kamata a yi wa Gbajabiamila wata kulawa ta musamman ba.

Kalaman Atiku sun biyo bayan zarge-zargen da shugaban PFIPC, Adeniyi Adeyemi, ya yi cewa Gbajabiamila ya karɓi cin hancin N400 miliyan domin samar masa da takardar naɗi a wani muƙami. Gbajabiamila ma na fuskantar wasu zarge-zargen da suka shafi kuɗaɗen kuɗin fito na harkar mai da iskar gas, sai dai har yanzu bai mayar da martani a hukumance kan zarge-zargen ba.

More from this stream

Recomended