Mai neman takarar shugaban kasa a jam’iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya kai ziyara kasar Amurka.
A cikin wasu hotuna da ya wallafa a shafukansa na soshiyal midiya Atiku ya sanar da cewa ya sauka a birnin Washington.
Ya kai ziyarar ne bisa amsa gayyatar da cibiyar kasuwancin Amurka ta yi masa.
A yayin ziyarar Atiku na tare da wasu jiga-jigan jam’iyar PDP.