Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, ya bayyana cewa tattaunawa tsakanin Amurka da Iran na fuskantar ƙalubale, inda ya ce yana kallon Iraniyawa a matsayin mutane masu taurin kai.
A wata hira da tashar Fox News, Vance ya ce akwai rarrabuwar kawuna a cikin shugabancin Iran. A cewarsa, wasu na goyon bayan ci gaba da tattaunawa, yayin da masu tsattsauran ra’ayi ke son a ci gaba da yaƙi.
Ya ce duk da ana samun ci gaba da koma baya a rikicin, yana da yakinin cewa daga ƙarshe “komai zai ƙare ne ta hanyar da za ta amfani al’ummar Amurka.”
A halin da ake ciki, wasu rahotanni sun ce shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, na iya kai ziyara Pakistan cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, sai dai gwamnatin Iran ba ta tabbatar ko musanta rahoton ba.
J.D. Vance: Rikicin Amurka Da Iran Na Fuskantar Ƙalubale

