An yi ƙone-ƙone a garin Lafiya kan hukuncin kotun ƙoli da ya tabbatar da zaɓen Abdullahi Sule

Wasu rukunin matasa sun fantsama kan tituna a ranar Juma’a inda suka gudanar da zanga-zangar nuna adawa da hukuncin kotun ƙoli da ya tabbatar da zaɓen, Abdullahi Sule a matsayin gwamnan jihar Nasarawa.

Gidan Talabijin na Channels ya rawaito cewa masu zanga-zangar sun ƙona tayoyi a gaban ginin ofishin jam’iyar PDP dake Lafiya.

Har ila yau masu zanga-zangar sun ƙona tayoyi akan babbar hanyar tafiya birnin Jos babban birnin jihar Filato.

Zanga-zangar ta jawo an rufe makarantu dama wuraren sana’a a birnin na Lafiya.

Tushen Abin Da Ya Faru

Biyo bayan ƙarar da ɗan takarar jam’iyar PDP a zaɓen gwamnan jihar, David Ombugadu ya shigar kotun sauraren kararrakin zaɓe ta tabbatar da shi a matsayin zaɓaɓɓen gwamnan jihar.

Gwamna Sule ya ɗaukaka ƙarar hukuncin inda kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar masa da nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar da aka yi.

Rashin gamsuwa da hukuncin kotun ɗaukaka karar ne ya sa Ombugadu ya ɗaukaka ƙara ya zuwa kotun ƙoli inda kuma a yau ta yanke hukuncin da ya bawa gwamna Sule nasara.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...