
Babbar kotun tarayya dake Abuja a ranar Litinin ta bayar da belin Bello Badejo shugaban ƙungiyar fulani makiyaya ta Miyatti Allah Kauta Gore ta kan kuɗi naira biliyan 2 da kuma kawo mutane biyu wanda za su tsaya masa.
Mai shari’a Inyang Ekwo a hukuncin da ya yanke kan belin ya bayar da umarnin cewa ɗaya daga cikin wanda za su tsaya masa dole ya gabatar da shedar biyan haraji na tsawon shekara uku kuma dole ya kasance mazaunin birnin tarayya Abuja.
Alkalin ya kuma bayyana cewa dole ɗaya daga cikin mutane ya zamo yana da kadara a birnin Abuja da darajarta ta kai biliyan biyu.
Ekwo ya kuma umarci Bodejo da ya ajiye fasfonsa na tafiye-tafiye a wurin magatakardan kotun kuma dole ba zai fita daga Najeriya ba sai da izinin kotun.
Alkalin ya kuma yarda cewa laifin da ake tuhumar Bodejo da aikatawa laifi ne da ake iya bayar da beli kuma kotun tana da ikon bayar da belin.
Ya dage sauraron karar ya zuwa ranar 5, 6 da kuma 7 ga watan Oktoba.
Ana tuhumar Bodejo ne da laifin almundahanar kuɗaɗe da yawansu ya kai dalar Amurka miliyan $2.63.

