Alhazan Najeriya 6,635 sun isa ƙasar Saudiyya

Jumullar alhazan Najeriya 6,635 ne suka isa ƙasar Saudiya bayan da jiragen dake jigilar alhazan su ka yi sawu 14 a yayin da aikin Hajji na Shekarar 2026 ke cigaba da kankama ka’in da na’in.

Alkaluma daga cibiyar hukumar aikin hajji ta kasa, NAHCON ne suka bayyana haka.

Aikin kwashe alhazan na bana ya fara ne a ranar 3 ga watan Mayu inda ake sa ran kwashe maniyata dubu 50,000 dai-dai da kason kujera da gwamnatin Saudiya ta bawa Najeriya.

Aikin rukunin farko na kwashe alhazan ya tafi dai-dai da yadda aka tsara inda alhazan suka riƙa tashi daga filayen jiragen sama na jihohi daban-daban kuma suke sauka a biranen Jeddah da Madina.

A ranar farko ta fara aikin jigilar jirage uku sun kwashe alhazai 1451 daga jihohin Kebbi, Kogi, Nasarawa a yayin daga bisani jirgi na huɗu ya tashi daga jihar Ogun dauke da alhazai 345 da kuma ma’aikata 70.

A ranakun da suka biyo baya an samu nasarar kwashe alhazan da suka fito daga jihohin Oyo, Kebbi, Jigawa da kuma Lagos

Kamfanonin da suke aikin jigilar alhazan sun haɗa da Air Peace, Umza, Flynass da Max Air.

More from this stream

Recomended