
Wasu mutane da suka gudanar da zanga-zanga a birnin tarayya Abuja sun bukaci gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya ceto yara ɗalibai yan makaranta da kuma malaman su dake hannun masu garkuwa da mutane.
Masu zanga-zangar sun mamaye gadar Nyanya-Karu dake Abuja domin gabatar da bukatunsu.
Zanga-zangar ta haifar da cunkoson ababen hawa a hanyar har sai da ta kai ga sojoji sun kawo ɗauki inda suka kawar da mutanen.
Masu zangar sun rika kiran ” Dole Tinubu ya sauka, ka dawo mana da yaranmu,” a yayin da suke ɗauke da kwalaye da aka rubuta a kuɓutar da yara da kuma malaman da aka ɗauke a jihohin Oyo da Borno.
Martins Vincent Otse da aka fi sani da Very Darkman wanda ke fafutuka a kafafen sadarwar na ɗaya daga cikin waɗanda suka shiga zanga-zangar.

