Tsohon dan takarar shugaban kasa kuma gogaggen dan jarida, Dele Momodu, ya bayyana cewa gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki na cikin fargaba sakamakon tasirin da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da kuma sabuwar hadakar jam’iyyun adawa ke samu.
Momodu ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a cikin shirin Politics Today na tashar Channels Television a ranar Litinin, inda ya ce “da zarar ka ga ana kamfe da batanci kan Atiku, to ka san suna jin tsoronsa.”
Ya kara da cewa: “Har dan uwana Bwala, na ji shi makonni da suka wuce yana rokon Atiku da ya shiga tafiyar Tinubu. Tun daga 1993 da ya janye wa uban gidana na siyasa, Atiku ya ci gaba da bin burinsa ba tare da samun taimakon gwamnoni ko kudin gwamnati ba. Ya kasance mai zuba jari a fannin ilimi da noma.
“A wurina, wannan misali ne na shugaba nagari da ya kamata a samu a Najeriya. Ba za ka ga ‘yan daba a kofar gidansa ba, kuma ba zai taba kiran mu da neman wanda za a sa a INEC don masa magudi ba. Wadannan abubuwa ne da nake darajanta a kansa, kuma ina da ‘yancin in bayyana ra’ayina.”
Dele Momodu ya kuma bayyana gamsuwarsa da cancantar Peter Obi a matsayin wanda zai iya jagorantar sabuwar hadakar jam’iyyun adawa.
Sai dai ya bukaci a yi amfani da tsarin dimokiradiyya wajen fitar da shugaban hadakar daga cikin Obi, Atiku da kuma Rotimi Amaechi.
Ya ce: “Ban taba ce wa kowa kada ya goyi bayan Obi ba. Obi abokina ne na musamman. Idan za a tambaye ni yau wanda ya dace ya jagoranci hadakar, zan ce Obi. Amma a matsayina na dan dimokiradiyya, ina fatan za su bi hanya ta dimokiradiyya wajen fitar da jagora domin kada a ce an tilasta wa mutane.”
Ya kuma kara da cewa: “Bari kowa ya fita ya yi kamfe — masu goyon bayan Obi su yi masa kamfe, masu Atiku su tsaya da shi, haka kuma masu Amaechi su tsaya da shi. Wannan shi ne ra’ayina, kuma bana ganin laifi a ciki.”
Dele Momodu ya ce yana alfahari da yadda hadakar ke tafiya, inda ya bayyana cewa unlike yadda APC ta fara a daidai lokacin da wasu ’yan siyasa kadan suka fice daga wasu jam’iyyu suka kafa jam’iyya guda, wannan tafiya da ake yi yanzu ta hadakar ’yan adawa wani gagarumin motsi ne, kuma “za ka iya ganin kamar guguwa ce ta fara tasowa.”
Gwamnatin APC Na Tsoron Atiku Abubakar Da Hadakar ‘Yan Adawa, A Cewar Dele Momodu
