Tsohon Sakataren Gwamnatin Borno Ya Rasu Kwanaki Kaɗan Bayan Ya Bar Aiki

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Borno, Alhaji Usman Jidda Shuwa ya riga mu gidan gaskiya.

Shuwa wanda har ranar 29 ga watan Mayu shi ne sakataren gwamnatin jihar ta Babagana Umara Zulum ya mutu bayan gajeriyar rashin lafiya.

A cewar wata majiya dake iyalan mamacin ya mutu ne a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

Shuwa kwararren ma’aikacin gwamnatin ne da ya yi aiki a gwamnatin tarayya da kuma ta jiha.

Ya rasu yana da shekaru 65.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]