
Aƙalla mutane 15 ne da ake zarginsu da kasancewa mayaƙan ƙungiyar ISWAP ne aka kashe a wani harin jirgin sama marar matuki a karamar hukumar Marte ta jihar Borno.
A cewar kafar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi dama Najeriya baki ɗaya an kai harin ne a ranar Talata da ƙarfe 05:35 na asuba bayan da bayanan sirri suka nuna mana cewa akwai ƴan ta’addan a wajejen yankin KLA Balia dake ƙaramar hukumar Marte.
Kafar yaɗa labaran ta bayyana cewa jirgin saman marar matuki dake tattara bayanan sirri wanda aka yi wa laƙabi da ” Guardian” shi ne ya gano wasu motoci uku da aka ɓoye su a wurare daban daban kafin daga bisani jirgin ya gano wasu mutane biyar da suka ɓuya a kasan bishiya.
Makama sun kara da cewa bayan jirgin ya tabbatar da mutanen sai ya harba musu bam inda ya kashe su nan take a yayin da fashewar wasu abubuwa a wurin ta yi asarar rayukan sauran mutanen hakan ya sa yawan waɗanda suka mutu ya ƙaru ya zuwa mutane 15.

