Tsohon Sakataren Gwamnatin Borno Ya Rasu Kwanaki Kaɗan Bayan Ya Bar Aiki

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Borno, Alhaji Usman Jidda Shuwa ya riga mu gidan gaskiya.

Shuwa wanda har ranar 29 ga watan Mayu shi ne sakataren gwamnatin jihar ta Babagana Umara Zulum ya mutu bayan gajeriyar rashin lafiya.

A cewar wata majiya dake iyalan mamacin ya mutu ne a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

Shuwa kwararren ma’aikacin gwamnatin ne da ya yi aiki a gwamnatin tarayya da kuma ta jiha.

Ya rasu yana da shekaru 65.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]