An kama sojan dake sayarwa da yan ta’adda kakin soja

Rundunar sojan Najeriya ta samu nasarar kama wani sojanta da ta sanar tana nema ruwa a jallo bayan da aka zarge da laifin sayarwa da yan ta’adda kakin soja.

Yusuf na aiki ne da masana’antar rundunar sojan dake Lagos wacce ke samar da kayayyaki na sojoji da suka haɗa da kaki, alamar mukami da sauransu.

A ranar Lahadi ne dakarun sojan suka samu nasarar kama Yusuf a birnin Maiduguri na jihar Borno a dai-dai lokacin da yake kokarin hawa mota ya tsere ya zuwa kasar Kamaru.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi Mohammed Goni mai rikon muƙamin mai magana da yawun rundunar Operation Hadin Kai ya ce an ayyana a neman Yusuf ruwa a jallo a ranar 23 ga watan Yuli kan laifin da ake zarginsa da aikatawa.

A cewar sanarwar an kama wanda ake zargin ne dai-dai lokacin da yake kokarin shiga motar zuwa Kamaru biyo bayan bayanan sirri da rundunar ta samu.

Sanarwar ta kara da cewa Yusuf zai cigaba da kasance a tsare a hannun rundunar har sai an kammala bincike kafin ya gurfana a gaban kotun soja.

More from this stream

Recomended