Ɗan majalisar jiha ya mutu bayan kwana uku da fara aiki

Garba Madami, mamba a majalisar dokokin jihar Kaduna ya mutu.

Madami dan jam’iyar PDP na wakiltar mazabar Chikun a majalisar ya mutu a wani asibiti dake Kaduna.

Ba’asan musabbabin mutuwarsa ba.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, David Madami ɗa ga marigayin ya ce mutuwar mahaifin nasa ta kaɗa shi sosai.

Marigayin ya kasance tsohon kwamishina kasafin kudi da tsare-tsare ya kuma taɓa rike muƙamin mashawarci kan harkokin siyasa ga tsohon gwamnan Kaduna, Patrick Ibrahim Yakowa.

Mutuwar ta sa na zuwa ne kwana uku bayan da aka rantsar da su a matsayin yan majalisa.

More News

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...