
’Yan bindiga sun kashe makiyaya biyu tare da jikkata wani mutum a wasu hare-hare da suka faru a Jihar Filato.
Hare-haren sun faru ne a Kpanchuku da ke Jebbu Bassa da kuma Gana Ropp, a wasu ƙananan hukumomin jihar.
Sakataren Ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) na Jihar Filato, Muhammad Salihu Isa, ya ce ɗaya daga cikin wadanda aka kashe, Sani Ibrahim mai shekaru 18, an farmake shi ne yayin da yake kiwon shanunsa.
Ya ce an kashe Asma’u Salihu, mai shekaru 15, a lokacin da maharan suka kai hari garinsu, yayin da suka kuma jikkata ɗan uwanta.
Isa ya yi Allah-wadai da hare-haren, inda ya bayyana su a matsayin mummunan lamari. Ya ce hare-haren sun yi sanadin asarar makiyaya da shanu da dama.
Ya yi kira ga jami’an tsaro da su gudanar da bincike tare da kama wadanda ke da hannu a hare-haren. Ya kuma bukaci makiyaya da sauran al’umma su kwantar da hankalinsu tare da guje wa ɗaukar doka a hannunsu.
Mahaifin Asma’u, Salihu Isa, ya ce maharan sun fara harbe-harbe jim kaɗan bayan sallar isha’i, inda suka kashe ’yarsa tare da jikkata ɗansa. Ya ce sun kai rahoton lamarin ga jami’an tsaro.
Kakakin rundunar Operation Enduring Peace, Kyaftin Polycarp Oteh, bai yi wani bayani kan lamarin ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoto.