Ƴan sanda sun cafke wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane a Abuja

Jami’an rundunar ‘yan sandan Najeriya sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne da ake kyautata zaton yana da hannu wajen yin garkuwa da Nabeeha, diyar wani lauya a Bwari.

Idan ba a manta ba ‘yan bindiga sun sace kimanin mutane 19 daga rukunin gidaje na Sagwari da ke unguwar Dutsen-Alhaji a karamar hukumar Bwari a babban birnin tarayya.

Masu garkuwa da mutanen sun bukaci a biya su N700m don sakin mutanen da suka kama.

Masu garkuwa da mutanen sun kashe hudu daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su, ciki har da Nabeeha Al-Kadriyar, daliba mai karatun digiri kuma ƴar aji 4 a fannin nazarin halittu a jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, da Folashade Ariyo ‘yar shekara 13.

An yi garkuwa da Nabeeha ne tare da wasu ’yan’uwanta shida.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...