Mutane 16 ciki har da wani Rabaran a ka sace a lokacin da wasu Æ´an bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka kai hari kan wasu Æ™auyuka uku dake Æ™aramar hukumar Zing ta jihar Taraba ranar Juma’a da daddare.
A cewar wasu majiyoyi dake yankin Æ´an bindigar su da yawa sun kai hari Æ™auyukan Dekko, Lama da Monkin ranar Juma’a da daddare inda suka yi garkuwa da mutane 16.
Mutanen ƙauyukan da dama sun samu raunin harbin bindiga lokacin da suke ƙoƙarin hawa saman tsaunuka a ƙoƙarin tserewa a lokacin harin ƴan bindigar.
Ƴan bindigar dake kan babura an ƙiyasta cewa yawansu ya kai 100.
Wata majiya dake yankin ta bayyana cewa ƴan bindigar wani ɓangare ne na ƴan fashin daji da sojoji da mafarauta suka kora daga wasu tsaunuka dake ƙaramar hukumar Yorro ta jihar.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar SP Usman Abdullah ya tabbatar da kai harin.