Kashim Shettima Ya Karɓi Gwamnan Taraba Da Magoya Bayansa Zuwa Jam’iyyar APC

Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Tinubu wajen karɓar Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, da magoya bayansa zuwa jam’iyyar APC a hukumance.

Bikin karɓar gwamnan ya gudana ne ranar Asabar a birnin Jalingo, fadar gwamnatin jihar.

A jawabin sa a wurin taron, Shettima ya ce jihar Taraba na ɗaya daga cikin jihohi mafi muhimmanci wajen samar da abinci, makamashi, da tsaro ga Najeriya.

Ya kara da cewa Shugaba Tinubu ya sanar wa gwamnan cewa yana da muhimmiyar rawa a cikin jam’iyyar APC, musamman wajen ciyar da jihar gaba.

Shettima ya ce:

“Abin da ya bambanta jam’iyarmu da sauran shi ne mu, mun yi imanin ƙasarmu za ta ci gaba da wanzuwa ne idan muka fahimci ƙarfinmu da yadda za mu taimaka, kuma mun tabbata jihar Taraba na ɗaya daga cikin ƙarfin ƙasarmu.”

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]