Kashim Shettima Ya Karɓi Gwamnan Taraba Da Magoya Bayansa Zuwa Jam’iyyar APC

Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Tinubu wajen karɓar Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, da magoya bayansa zuwa jam’iyyar APC a hukumance.

Bikin karɓar gwamnan ya gudana ne ranar Asabar a birnin Jalingo, fadar gwamnatin jihar.

A jawabin sa a wurin taron, Shettima ya ce jihar Taraba na ɗaya daga cikin jihohi mafi muhimmanci wajen samar da abinci, makamashi, da tsaro ga Najeriya.

Ya kara da cewa Shugaba Tinubu ya sanar wa gwamnan cewa yana da muhimmiyar rawa a cikin jam’iyyar APC, musamman wajen ciyar da jihar gaba.

Shettima ya ce:

“Abin da ya bambanta jam’iyarmu da sauran shi ne mu, mun yi imanin ƙasarmu za ta ci gaba da wanzuwa ne idan muka fahimci ƙarfinmu da yadda za mu taimaka, kuma mun tabbata jihar Taraba na ɗaya daga cikin ƙarfin ƙasarmu.”

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]