Falana Ya Gargadi Gwamnatoci Kan Tattaunawa Da ’Yan Ta’adda



Fitaccen lauya mai kare hakkin bil’adama, Femi Falana, ya gargadi gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi da su daina tattaunawa ko ba da lada ga ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga.

Falana ya bayyana hakan ne yayin taron shekara-shekara na kungiyar Amnesty International da aka gudanar a Abuja.

Ya yi zargin cewa wasu jami’an gwamnati suna ganawa da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga, lamarin da ya kai ga yafewa wasu daga cikinsu tare da ba su kudade bayan sun nuna tuba.

Falana ya ce kungiyoyin ta’addanci irin su Boko Haram an haramta su a karkashin dokar hana ta’addanci ta Najeriya, don haka ya kamata a gurfanar da mambobinsu a gaban kotu maimakon yi musu afuwa.

Ya kuma bayyana cewa dokar ta tanadi hukuncin daurin akalla shekara ashirin ga duk wanda aka samu da hannu wajen shirya taro, bayar da tallafi ko mu’amala da kungiyoyin ta’addanci.

More from this stream

Recomended