Ƴan bindiga sun yi garkuwa da mata 8 Abuja

Wasu mata 8 ne aka yi garkuwa da su dai-dai lokacin da suke aiki a wata gona dake kauyen Gwombe dake ƙarƙashin masarautar Gwargwada a karamar hukumar Kuje ta birnin tarayya Abuja.

Sace matan na zuwa ne kasa da sa’o’i 48 bayan da wasu yan bindiga suka sace mahaifin mataimakin shugaban karamar hukumar Kwali tare da wasu mutane 6 a kauyen Yawuti dake karamar hukumar Kwali dake Abuja.

Wani mazaunin Gwargwada, Usman Yakubu ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe biyar na yammacin ranar Litinin.

Ya ce matan dukansu matan aure ne kuma ƴan bindigar ɗauke da bindigar AK-47 sun kewaye su a cikin gonar kana suka yi awon gaba da su.

Wani mai riƙe da sarautar gargajiya a ƙauyen da ya nemi a sakaya sunansa ya ce huɗu daga cikin matan sun fito ne daga gida guda.

More News

Matatar mai ta fatakwal za ta iya fara aiki a ƙarshen watan Yuni

Matatar mai ta Fatakwal mai tace mai ganga 210,000 a kowacce rana na iya fara aiki a karshen watan Yuli bayan dogon lokaci. Jami’in hulda...

Peter Obi Ya Ziyarci Mutanen Da Su Ka Ƙone Sakamakon Wutar Da Wani Ya Cinnawa   Masallaci A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa  a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyar Labour Party (LP) Peter Obi ya ziyarci mutanen da wani matashi ya cinnawa wuta a...

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...