Ƴan Bindiga Sun Kashe Mai Magana Da Yawun Jam’iyar APC A Jihar Filato

Wasu da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Sylvanus Namang  mai magana da yawun jam’iyar APC ta jihar Filato a garin Pankshin dake ƙaramar hukumar Pankshin ta jihar Filato.

Wani jigo a jam’iyar ta APC da ya nemi a ɓoye sunansa ya faɗawa jaridar Daily Trust cewa marigayin ya mutu ne sanadiyyar raunukan da ya samu a harin da aka kai masa.

Ya bayyana marigayi Namang a matsayin aboki abun dogaro wanda ya mayar da hankali matuƙa wajen cigaban jam’iyar APC a dukkanin matakai inda ya ƙara da cewa jam’iyar za ta fitar da sanarwa nan gaba kaɗan  kan mutuwarsa.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa an kashe marigayin ne a wajen ɗakinsa na otal da misalin ƙarfe 07:30 na safe bayan da wasu ƴan bindiga suka buɗe masa wuta.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa marigayin ya bar gida ranar Asabar domin halartar bikin jana’iza a garin na Pankshin.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...