
Fulani makiyaya da basu gaza uku ba aka kashe tare da jikkata wasu biyu a wani sabon farmaki da aka kai a wajejen kauyen Bangai dake ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato.
Yahaya Musa, sakataren kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria a Riyom shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya kara da cewa shanu 14 aka kashe a yayin da aka jikkata wasu 4.
Musa ya ce lamarin ya faru ne a dai-dai lokacin da makiyayan ke kiwon dabbobinsu a yankin.
Al’ummar Fulani makiyaya sun yi allawadai da harin inda suka yi kira ga jami’an tsaro da su gano wadanda suka aikata laifin tare da gurfanar da su gaban shari’a.
Fulani makiyaya dake ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato sun yi allawadai da harin da su ka ce ya faru da misalin ƙarfe 02:30 na ranar 6 ga watan Agusta.
Sakataren kungiyar ta MACBAN ya yi zargin cewa maharan da suka kai hari yan kabilar Berom ne dake ɗauke da makamai kuma sun fito ne daga Anguwan Weren dake mazabar Rim.
A cewar Musa waɗanda aka kashe sun hada da Isma’il Idris mai shekaru 15, Hamza Aminu mai shekaru 17, Ja’afar Umar mai shekaru 27 a yayin da Ango Ibrahim mai shekaru 14 da kuma Abdullahi Buhari mai shekaru 20 suka samu raunukae inda suke kwance a asibiti.

