Zulum ya raba tallafin abinci na gwamnatin tarayya ga gidaje 10,000 a Mafa

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya jagoranci rabon tallafin abinci da gwamnatin tarayya ta bayar ga iyalai sama da 10,000 a karamar hukumar Mafa.

An gudanar da rabon kayayyakin ne a ranar Talata a cibiyoyi hudu da ke garin Mafa, hedikwatar karamar hukumar.

Kowanne daga cikin masu gidaje 10,000 ɗin ya samu tallafin da ya kunshi buhun masara mai nauyin kilogiram 50.

Zulum ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin tarayya bisa wannan shiga tsakani da aka yi, ya kuma bayyana cewa an raba wasu kayan abinci a Gwoza da Nganzai.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]