‘Yan Fashi Sun Hallaka Wani Mutumi Da Adda a Kano

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta tabbatar da cafke wani matashi mai shekaru 20 da haihuwa, Aliyu Umar, bisa zarginsa da hannu a kisan wani mutum a unguwar Danbare da ke karamar hukumar Gwale.

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata. Ya ce lamarin ya faru da safiyar Litinin, 5 ga Mayu, da misalin karfe 6:40 na safe.

“A wannan rana ne wasu ‘yan fashi guda biyu suka kutsa gidan wani Shehu Muhammad mai shekaru 30 da haihuwa, suka kai masa hari da wata babbar adda mai kaifi, suka yi masa raunuka da dama a jiki,” in ji Kiyawa.

Ya kara da cewa bayan samun rahoton aukuwar lamarin, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, PhD, ya tura jami’an sintiri da masu bincike zuwa wurin da aka aikata laifin.

An garzaya da Shehu Muhammad zuwa Asibitin Musamman na Murtala Muhammad domin samun kulawar likita, amma daga bisani likita ya tabbatar da mutuwarsa.

Jami’an tsaro sun samu nasarar kama daya daga cikin wadanda ake zargi, Aliyu Umar, a wurin da aka kai harin, kuma an kwato makamin da aka yi amfani da shi wajen aikata laifin.


Rundunar ‘yan sandan ta yaba da irin hadin kai da goyon bayan da al’ummar yankin suka bayar wajen cafke wanda ake zargi, tana kuma bukatar jama’a su ci gaba da kai rahoton duk wani motsi ko hali da ke da alamun zama barazana.

More from this stream

Recomended