Yan bindiga sun yi garkuwa da amarya sa’o’i kaɗan kafin a daura mata aure

Wasu da ake zargin yan bindiga ne sun kai farmaki kauyen Chacho dake karamar hukumar, Wurno ta jihar Sokoto inda suka dauke wata amarya da kawayenta yan sa’o’i kadan kafin a daura mata aure.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun farma kauyen da misalin karfe 1:30 na daren ranar Lahadi inda suka yi awon gaba da amaryar, kawayenta da kuma wasu mazauna kauyen su 8.

Dukkanin wadanda aka sace din mata ne sai namiji guda ɗaya. Har ila yau an jikkata mutum guda a harin.

A cewar wani mazaunin kauyen da ya nemi a boye sunansa ya ce abin da ya faru ya daga musu hankali.

“Munyi bakin ciki da abun da yafaru da safiyar yau yakamata ayi daurin auren yarinyar.amma aka dauke ta tare da  kawayenta wadanda za su yi mata yan matan amarya,” ya ce

Ya kara da cewa anyi garkuwa da wasu mata 7 da kuma wani namiji ɗaya a lokacin farmakin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]