Yan bindiga sun yi garkuwa da amarya sa’o’i kaɗan kafin a daura mata aure

Wasu da ake zargin yan bindiga ne sun kai farmaki kauyen Chacho dake karamar hukumar, Wurno ta jihar Sokoto inda suka dauke wata amarya da kawayenta yan sa’o’i kadan kafin a daura mata aure.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun farma kauyen da misalin karfe 1:30 na daren ranar Lahadi inda suka yi awon gaba da amaryar, kawayenta da kuma wasu mazauna kauyen su 8.

Dukkanin wadanda aka sace din mata ne sai namiji guda ɗaya. Har ila yau an jikkata mutum guda a harin.

A cewar wani mazaunin kauyen da ya nemi a boye sunansa ya ce abin da ya faru ya daga musu hankali.

“Munyi bakin ciki da abun da yafaru da safiyar yau yakamata ayi daurin auren yarinyar.amma aka dauke ta tare da  kawayenta wadanda za su yi mata yan matan amarya,” ya ce

Ya kara da cewa anyi garkuwa da wasu mata 7 da kuma wani namiji ɗaya a lokacin farmakin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]