Yan bindiga sun sace mutane da dama a Zamfara

Wasu yan bindiga da aka bada rahoton sun yi shigar mata sun kai hari karamar hukumar Maru inda suka sace mutane da ba a san dadinsu ba.

A cewar mazauna yankin yan bindigar sun kai farmaki ne da wajen karfe 7 na dare akan babura inda suka fara harbi kafin su yi awon gaba da mutane ciki har da mata da yara.

Kauyen da aka kai harin na da tazarar kilomita 30 daga karamar hukumar Bungudu inda yan bindiga suka sace mutane 7 a ranar Lahadi ciki har É—an sarki.

“Ƴan ta’addar sun farma garin babu jimawa da idar da sallar Magriba inda suka fara harbin kan me uwa da wabi. Mutane sun fara gudun tsira inda yan bindigar suka bi su cikin gidajensu i suka yi awon gaba da yawa daga cikinsu.” a cewar wata majiya dake garin.

Majiyar ta kara da cewa duk da cewa ba a san yawan mutanen da suka tafi da su ba yan bindigar sun tafi da akalla mutane 50.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...