Yan bindiga sun kashe wani Fasto a Kogi

Yan bindiga sun kashe, Jacob Wodi Hulobu Faston cocin Living Faith dake Aloko-Oganenigu dake ƙaramar hukumar Dekija a jihar Kogi.

Wasu yan bindiga ne da ba a san ko su waye ba suka kai hari kan farmaki kan kauyen a ranar Lahad.

Rahotanni sun nuna cewa faston ya samu nasarar tserewa tare da mabiyansa a yayin harin yan bindigar dai-dai lokacin da suke da tsaka da taron addu’a da asubahi.

A cewar wani mambam cocin mai suna Samuel faston ya koma ne yaga halin da cocin take ciki bayan da kura ta lafa inda anan yan bindigar suka kashe shi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]