Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani malami a Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Anka a Jihar Zamfara, Mustapha Yahaya Maru, duk da cewa iyalansa sun biya kuɗin fansa domin a sake shi.
Rahotanni sun ce an sace malamin ne a farkon watan nan yayin da yake tafiya zuwa Anka tare da wasu fasinjoji bayan ’yan bindigar sun tare motarsu a hanya.
Bayan tattaunawa da iyalansa, maharan sun karɓi kuɗin fansa amma daga bisani suka kashe shi a ranar Talata.
Lamarin ya jefa al’ummar Maru da iyalansa cikin alhini tare da ƙara tayar da hankula kan matsalar tsaro a Zamfara da sauran yankunan Arewa maso Yamma.
A wani harin daban kuma, wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai hari kan matafiya a hanyar Tashar Lawali da ke ƙaramar hukumar Talata Mafara. Rahotanni sun ce maharan sun kashe direba mai suna Lawali Hakimi tare da sace jami’an ƙaramar hukuma biyu, yayin da wani jami’i ya samu raunin harbin bindiga a hannu.
‘Yan Bindiga Sun Kashe MaIamin Makaranta Bayan Karɓar Kuɗin Fansa A Zamfara

