Wata kungiya ta yi zanga-zangar goyon bayan INEC kan matakin da ta ɗauka akan jam’iyar ADC

Wata kungiya mai zaman kanta dake Abuja ta jagoranci zanga-zangar nuna goyon baya ga hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC kan matakin da ta dauka game da jam’iyar adawa ta ADC.

Kungiyar mai suna Concern Nigerian Youth Forum ta gudanar da zanga-zangar ne a ofishin hukumar ta INEC dake Abuja.

Shugaban kungiyar Adeyeye Olugbenga ya ce sun gudanar da zanga-zangar domin kare da dimakwaradiya da kuma mutuncin hukumar ta INEC.

Ya ce zanga-zangar ta zama dole duba da yadda hukumar INEC ke fuskantar suka daga wasu mutane tun bayan da ta aiwatar da hukuncin kotu da ya soke shugabancin jam’iyar ta ADC.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]