Wata kungiya ta yi zanga-zangar goyon bayan INEC kan matakin da ta ɗauka akan jam’iyar ADC

Wata kungiya mai zaman kanta dake Abuja ta jagoranci zanga-zangar nuna goyon baya ga hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC kan matakin da ta dauka game da jam’iyar adawa ta ADC.

Kungiyar mai suna Concern Nigerian Youth Forum ta gudanar da zanga-zangar ne a ofishin hukumar ta INEC dake Abuja.

Shugaban kungiyar Adeyeye Olugbenga ya ce sun gudanar da zanga-zangar domin kare da dimakwaradiya da kuma mutuncin hukumar ta INEC.

Ya ce zanga-zangar ta zama dole duba da yadda hukumar INEC ke fuskantar suka daga wasu mutane tun bayan da ta aiwatar da hukuncin kotu da ya soke shugabancin jam’iyar ta ADC.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]