Trump Ya Ce An Samu Gagarumin Ci Gaba A Tattaunawar Iran Da Amurka



Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ana samun ci gaba mai kyau a tattaunawar da ake yi tsakanin Amurka da Iran kan shirin nukiliyar Tehran.

Trump ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ganawa da manema labarai kafin tafiyarsa zuwa jihar North Dakota.

Ya ce tarukan da aka gudanar a Qatar cikin kwanakin nan sun kasance masu amfani, inda ya ƙara da cewa tsarin da ake bi wajen wargaza shirin nukiliyar Iran yana tafiya yadda ya kamata.

“Muna da kyakkyawar fahimta da juna,” in ji Trump.

Sai dai Iran ta sake jaddada cewa shirinta na nukiliya na zaman lafiya ne kawai, ba don ƙera makaman yaƙi ba.

A halin yanzu, ana ci gaba da tattaunawar ba na kai-tsaye ba tsakanin ƙasashen biyu a Doha na ƙasar Qatar, tare da shiga tsakani daga Qatar da Pakistan.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]