Sojojin Najeriya sun kuɓutar da matar marigayi Janar Rabe Abubakar

Dakarun sojan ƙasan  Najeriya tare da haɗin gwiwar dakarun sojan saman Najeriya sun samu nasarar ceto matar marigayi Janar Rabe Abubakar daga hannun ƴan bindiga.

Kuɓutar da matar na zuwa ne kwanaki biyu kenan bayan jana’izar marigayi Janar Rabe wanda  ya mutu a hannun ƴan bindigar da su ka yi garkuwa da shi a jihar Katsina.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin ma’aikatar tsaron Najeriya ta bayyana cewa an samu nasarar ceto matar ne biyo zafafawa tare da fadada bincike da aikin ceto da  dakarun rundunar Operation Fansan Yamma su ka yi.

A yayin binciken ne dakarun su ka yi arangama da ƴan bindigar wajen ƙauyen Tungar Yamma abun da ya kai ga kuɓutar da matar marigayin.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce matar marigayin ta samu raunin harbin bindiga kuma tuni aka garzaya da ita ya zuwa asibitin sojoji inda take samun kulawa.

Sanarwar ta cigaba da cewa sojojin za su cigaba da bin diddigin waɗanda suka yi garkuwar da su har sai sun ga bayansu.

More from this stream

Recomended