Sojoji sun yi luguden wuta wa ƴan ta’adda a Kaduna

Rundunar sojin sama ta Najeriya NAF ta ce ta kashe ‘yan ta’adda da dama a Tsauni Doka da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Ya ce rundunar ta NAF na Operation Whirl Punch ce ta kai harin.

Mista Gabkwet ya ce an kai harin ne bayan wasu sahihin bayanan sirri sun nuna akwai wani shugaban ‘yan ta’adda da aka fi sani da Boderi da sojojinsa a Tsauni Doka.

Ya ce an kai hare-haren ta sama a wurin da sanyin safiyar ranar 16 ga watan Nuwamba, wanda ya haifar da mummunan sakamako ga ‘yan ta’addar.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...