
Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami’anta sun kama wasu mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma fashi da makami a jihar Kaduna dama makotan jihohi.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Talata, Anthony Placid ya ce mutanen da aka kama Yusuf Rabo da Musa Adamu an kama su ne biyo bayan binciken da aka gudanar na yin garkuwa da wani mai suna, Alhaji Rabo Jelani.
Placid ya ce binciken da aka gudanar ya nuna cewa Yusuf Rabo ya haɗa baki da Adamu da kuma Ali Haruna wanda ake nema ruwa a jallo inda suka ɗauke dattijon saboda hasashen yana da dukiya da shanu.
Binciken da aka gudanar ya nuna mutanen sun mallaki bindigogi ƙirar AK-47 inda su ka yi amfani da su a lokuta da daban-daban wajen aikata fashi da kuma yin garkuwar.
Sun rika kai mutanen da suka yi garkuwa da su ya zuwa cikin daji kafin Yusuf Rabo da kansa ya cimma yarjejeniyar kuɗin fansa.
Mai magana da yawun rundunar ya kara da cewa mutanen su ne da alhakin yin garkuwa da wani ɗan kasuwa mai suna Iyke.

