An ba wa ɗan sanda kyautar naira miliyan 1 saboda ƙin karɓar cin hanci

Shugaban Karamar Hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna, Hon. Nasara Rabo, ya bai wa wani jami’in ‘yan sanda, Difi’o Idris Ibrahim, zunzurutun kudi har naira miliyan 1, bisa ƙin amincewa da wasu maƙudan kudade da wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ya bayar domin kar a bincike shi.

Rabo wanda ya bayyana hakan a cikin wata takardar shawarwarin da ya fitar a ranar Litinin din da ta gabata ya bayyana cewa DPO din ya kama wani mai garkuwa da mutane a ranar 22 ga watan Janairun 2024, wanda ya yi yunkurin ba shi cin hanci da makudan kudade domin a datse binciken ko kuma a murguda aikin binciken.

Amma ɗan sandan ya ki amincewa da cin hancin kuma ya sha alwashin ba da damar doka ta yi aiki yadda ya kamata saboda kishin ƙasa da kuma tsayin daka wajen tabbatar da adalci.

“Wannan kokari na musamman da kuka yi ba iya alfahari rundunar ‘yan sandan Najeriya suka yi ba, har ma ya sanya mutanen karamar hukumar Kagarko, na jihar Kaduna, da Najeriya baki daya, ya kara da cewa wannan shaida ce da ta dace.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]