Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin karbar kayan abinci da gwamnatin jihar ta raba a wani bangare na tallafin lalacewar tattalin arziki.

Wadanda lamarin ya rutsa da su, kuma wadanda har yanzu ba a bayyana sunayensu ba, abin ya rutsa da ne a safiyar Juma’a, wanda ya yi sanadiyyar jikkatar su.

Wata majiya ta bayyana cewa daliban da suka mutu mata ne, yayin da wasu da dama suka samu raunuka daban-daban a yayin da lamarin ya faru a dandalin Convention dake harabar jami’ar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]