Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi sani da Sunday Igboho, bisa zargin yi wa Fulani barazana a wani faifan bidiyo.

A ranar Litinin, dan a-waren ya shaida wa magoya bayansa cewa kada su jira gwamnatin kasar kafin ta dauki matakin yaki da Fulani makiyaya, wadanda ya yi zargin suna hana manoman yankin shiga gonakinsu a yankin Kudu maso Yamma.

“Wannan yanki ne namu. Mu kubutar da kanmu daga hannun Fulani. Ya kamata mu sanya tsaro a duk ƙasar Yarbawa. Ba mu buƙatar jiran kowa, har da gwamnati. Idan da gaske muke yi , bai kamata mu jira gwamnati ba, in ba haka ba Fulani za su ƙwace filayenmu gaba daya. Ya kamata mu kasance da haɗin kai. Wadanne gonaki ne muke da su kuma a kasar Yarbawa?  Za mu iya zuwa gona a yanzu?”, Mista Igboho ya ce.

Da yake mayar da martani ga sanarwar, shugaban kungiyar ta MACBAN na kasa, Baba Othman Ngelzarma, ya yi kira da a kama Mista Igboho tare da gurfanar da shi a gaban kuliya saboda ya yi “kalamai na cin amanar ƙasa.”

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...