Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudi ta jihar da ta miÆ™a mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru El-Rufai ta ciwo.

BuÆ™atar da majalisar ta miÆ™a na zuwa ne dai-dai lokacin da majalisar  ke cigaba da bincike kan sha’anin kuÉ—in jihar a zamanin mulkin na El-Rufai.

El-Rufai ya mulki jihar daga shekarar 2015 da 2023.

A ranar Talatar da ta wuce majalisar ta kafa kwamitin da zai binciki gwamnatin El-Rufai.

Kwamitin mai wakilai 13 an É—ora masa alhakin binciken basussuka, tallafin kuÉ—aÉ—e da kuma ayyukan da aka aiwatar daga shekarar 2015 ya zuwa 2023.

A wata wasiÆ™a mai É—auke da kwanan watan 22 ga watan Afrilu da akawun majalisar Sakinatu Idris ta sawa hannu kuma aka  aikewa kwamishinan kuÉ—in jihar ta nemi bayanai da ya shafi biyan Æ´an kwangilar kuÉ—in kwangiloli a zamanin mulkin El-Rufai.

A ranar 30 ga watan Maris ne gwamnan jihar,Mallam Uba Sani ya ce gwamnatinsa ta gaji bashin dala miliyan $587 bashin biyan ayyukan Æ´an kwangila 115.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...