Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar Kuntau dake ƙaramar hukumar Gwale ta jihar Kano.
Ginin ya ruguzo ne lokacin da ake tsaka da aiki da safiyar ranar Juma’a amma kuma ba’asan musabbabin rushewarsa ba.
AÆ™alla ma’aikata 11 ake fargabar sun maÆ™ale cikin baraguzai lokacin da lamarin ya faru.
Jami’in tsare-tsare na hukumar ta NEMA a Kano, Nuraddeen Abdullahi ya tabbatarwa da Kamfanin Dillancin Labarai Na Najeriya NAN cewa an samu nasarar ceto mutane biyu a dai-dai lokacin da suka tuntube shi.
Ya ƙara da cewa cikin mutane biyar da aka zaƙulo likitoci a Asibitin Murtala sun tabbatar da mutuwar uku daga ciki a yayin da biyu suka samu raunuka.