Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar Kuntau dake ƙaramar hukumar Gwale ta jihar Kano.

Ginin ya ruguzo ne lokacin da ake tsaka da aiki da safiyar ranar Juma’a amma kuma ba’asan musabbabin rushewarsa ba.

AÆ™alla ma’aikata 11 ake fargabar sun maÆ™ale cikin baraguzai lokacin da lamarin ya faru.

Jami’in tsare-tsare na hukumar ta NEMA a Kano, Nuraddeen Abdullahi ya tabbatarwa da Kamfanin Dillancin Labarai Na Najeriya NAN cewa an samu nasarar ceto mutane biyu a dai-dai lokacin da suka tuntube shi.

Ya ƙara da cewa cikin mutane biyar da aka zaƙulo likitoci a Asibitin Murtala sun tabbatar da mutuwar uku daga ciki a yayin da biyu suka samu raunuka.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...