Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar ɗaliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar ƙyanda.

A wata sanarwa ranar Litinin, A’isha Umar babbar sakatariyar ma’aikatar ilimi ta jihar ta ce an tsawaita hutun ɗaliban ne domin gwamnati ta samu damar yiwa dukkanin yaran jihar allurar riga-kafi.

Ta bayyana rashin jin ɗaɗin ta kan damuwar da hakan zai kawo inda ta bayyana cewa  wasu daga cikin yaran sun riga sun kamu da cutar.

Tun da farko an shirya cewa makarantu jihar ta Adamawa za su fara zangon karatu na uku ranar 06 ga watan Mayu amma yanzu aka ɗaga zuwa ranar 13 ga watan Mayu.

A cikin watan Afrilu aka bada rahoton mutuwar yara 19 a ƙaramar hukumar Mubi ta jihar sakamakon cutar ta ƙyanda.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...