![](https://arewa.ng/storage/screenshot_2024-05-17-21-28-58-406-edit_com4593039369528319133-1024x786.jpg)
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a ƙaramar hukumar Gezawa ta jihar ya ƙaru zuwa mutane 15.
A ranar Laraba ne aka tabbatar da mutuwar mutum guda a yayin da wasu 24 suka jikkata bayan da wani matashi ya watsa fetur ya kuma cinna musu wuta.
Abdullahi Haruna Kiyawa mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar ya ce matashin da ake zargi da cinna wutar mai suna, Shafi’u Abubakar ya ce ya yi haka ne saboda rikicin gado shi da danginsa.
A ranar Alhamis mai magana da yawun rundunar ya ce mutanen da suka mutu sun ƙaru daga 1 daga ɗaya ya zuwa 6.
Sai dai kwamishinan Æ´an sandan jihar, Usaini Gumel a ranar Juma’a ya ce Æ™arin wasu mutanen sun mutu lokacin da suke samun kulawar likitoci a Asibitin Murtala dake Kano.