Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban birnin jihar Niger.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Wasiu Abiodun mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar Niger ya ce ana amfani da ginin ne a matsayin rumbun ajiye kayayyaki.
Ya ce ginin ya ruguzo ne da misalin Æ™arfe 2:30 na ranar Juma’a.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu mutane da ba a san yawansu ba ne ake tunanin baraguzan ginin ya binne su.
Abiodun ya ce biyu daga cikin mutanen da aka ceto sun samu karamin rauni.
An kai waÉ—anda aka ceto ya zuwa Babban Asibitin Minna domin samun kulawar likita.