An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban birnin jihar Niger.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Wasiu Abiodun mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Niger ya ce ana amfani da ginin ne a matsayin rumbun ajiye kayayyaki.

Ya ce ginin ya ruguzo ne da misalin ƙarfe 2:30 na ranar Juma’a.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu mutane da ba a san yawansu ba ne ake tunanin baraguzan ginin ya binne su.

Abiodun ya ce biyu daga cikin mutanen da aka ceto sun samu karamin rauni.

An kai waɗanda aka ceto ya zuwa Babban Asibitin Minna domin samun kulawar likita.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]